Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, ministan shari'a na kasar Denmark Peter Humelgaard ya fada a ranar Laraba cewa: Al'amurran da suka shafi kona kur'ani a cikin 'yan kwanakin nan sun yi tasiri a kan barazanar da ake fuskanta. Muna cikin yanayi mai haɗari wanda ke buƙatar ƙarin kula da kan iyakoki don tunkarar barazanar da Denmark ke fuskanta.
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Denmark ta sanar a cikin wata sanarwa cewa: 'Yan sandan kasar Denmark sun sanar da ma'aikatar shari'a tare da shawarar hukumar leken asirin cewa a ra'ayinsu ya zama dole a ci gaba da karfafa ikon kan iyakar Denmark.
Wadannan ayyuka na kula da kan iyakar Sweden da Jamus, wadanda ya kamata a ci gaba da su har zuwa ranar 13 ga watan Agusta, za su ci gaba har zuwa ranar 17 ga watan Agusta.
A baya-bayan nan a kasashen Sweden da Denmark an sha yin ta'azzarar zagin kur'ani mai tsarki a gaban ofisoshin jakadancin kasashen musulmi, wanda baya ga kiran da jami'an diflomasiyyar kasashen biyu suka yi a hukumance, lamarin da ya janyo cece-kuce daga mutane a kasashen Larabawa da Musulunci.