Shafin yada labarai na The Will Najriya ya bayar da rahoton cewa, magoya bayan bayan Harka Islamiyya a Najeriya sun yi tir da Allawadai da wannan fim mai suna Fatal Arrogance, wanda a cikinsa ake kokarin bata fuskar harka Islamiyya, tare da nuna ta a matsayin wani gungu na 'yan ta'adda.
Wani fitaccen dan fina-finan Nollywood mai suna Pete Edochie ne ya fito a matsayin babban tauraroa acikin fim din inda yake a matsayin jagoran harka Islmiyya a cikin fim din.
Shugaban dandalin yada labarai na harka Islamiyya Ibrahim Musa ya fitar da wani bayani, wanda a cikinsa ya bayyana wannan fim din a matsayin cin zarafi, wanda zai iya haifar da babbar matsala a kasar, a kan haka ya bukaci Nollywood da su sake yin nazari kan fim din tun kafin su fito da shi.
3922618