Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, kakakin ma'aikatar harakokin wajen Jodan Sufyan Salman Al-Kudat na cewa kasarsa ta kira jakadan Isra'ila tare da mika masa wasikar nuna rashin amincewa da hare-haren baya-bayan da dakarun Isra'ila suka kai kan masallacin Qudus, sannan sun bukaci Isra'ila da ta kawo karshen harin wuce gona da irin da take kaiwa kan masallacin.
Al-Kudat ya kara cewa kasarsa ta yi tir da rufe kofofin masallacin na Qudus da kuma yadda dakarun haramtacciyar kasar Isra'ila ke hana Falastinawa shiga masallacin, tare da neman Isra'ila ta yi aiki da alkawarin da ta dauka na bin dokokin kasa da kasa.
Wannan mataki da kasar Jodan ta dauka na zuwa ne , bayan furicin da ministan tsaron cikin gidan Isra'ila ya yi na cewa lokaci ya yi da za a canza yanayin masallacin Qudus ta yadda Yahudawa za su samu damar shiga ciki, su kuma gudanar da ibadunsu .